Nijar
An tarwatsa mayakan Boko Haram a Nijar
An yi nasarar tarwatsa mayakan kungiyar Boko Haram da ke tayar da hankali, ta hanyar kai munanan hare hare da suka yi sanadiyar mutuwar mutane da dama a yankin kudu maso gabashin Jamhuriyar Niger.
Wallafawa ranar:
Talla
An kadammar da farmakin ne kan mayakan da tun cikin shekarar 2015 suka soma kai hare-haren, kamar yadda ministan cikin gidan kasar ta Niger Bazoum Mohamed, ya sanar.
Daukar wannan matakin ya biyo bayan babban kutse da dakarun Nigeriya suka yi a dajin Sambisa inda suka tarwatsa sansanin karshe da ya rage a hannun mayakan na Boko Haram.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu