Kamaru-Boko Haram
Dan kunar bakin wake ya kashe mutane biyu a Kamaru
Wani dan kunar bakin wake ya tarwatsa kansa tare da kashe mutane biyu a garin Mora da ke yankin arewacin Kamaru. Ana kyautata zaton cewa dan kunar bakin waken na kokarin isa ga wani wuri ne inda jama’a ke taron addu’o’in Kirismeti.
Wallafawa ranar:
Talla
Gwamnan yankin arewa mai nisa Midjiyawa Bakari ya tabbatar da mutuwar mutane biyu da suka hada da wani dalibi dan shekara 19.
Sannan harin da aka kai a Mora ya raunana wasu mutane biyar.
Kamaru dai na cikin kasashen da ke fama da ta’addancin kungiyar Boko Haram na Najeriya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu