Isa ga babban shafi
Gambia

MDD ta bukaci Jammeh ya mika mulki

Kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ya bukaci shugaban Gambia, Yahya Jammeh da ya mika nulki ga Adama Barrow da ya yi nasara a zaben da aka gudanar a farkon watan Disamba.

Shugaban Gambia Yahya Jammeh ya yi amai ya lashe, in da ya ki amincewa da shan kayi a zaben shugabancin kasar da aka gudanar a farkon watan Disamba
Shugaban Gambia Yahya Jammeh ya yi amai ya lashe, in da ya ki amincewa da shan kayi a zaben shugabancin kasar da aka gudanar a farkon watan Disamba REUTERS/Thierry Gouegnon
Talla

Wannna na zuwa ne bayan Jammeh ya sanar da kin amincewa da shan kayi, in da ya zargi jami’an hukumar zaben kasar da tafka kura-kurai.

Wata sanarwar da mambobin kwamitin 15 suka fitar, ta bukaci Jammeh da ya mutunta muradun ‘yan kasarsa kamar dai yadda ya yi a ranar 2 ga watan Disamban, in da ya amince da shan kayi.
 

Ministan harkokin wajen Senagal ne, Mankeur Ndiaye ya bukaci kwamitin tsaron da ya tsoma baki cikin lamarin.

A bangare guda, shugaban Jammeh ya hana jirgin shugabar kungiyar kasashen ECOWAS kuma shugabar kasar Liberia Ellen Johnson Sirlef sauka a cikin kasarsa, yayin da ya girke jami’an tsaro akan tituna.

Zababben shugaban kasar, Adama Barrow ya yi kira ga al'ummar kasar da su kwantar da hankulansu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.