Jam'iyyun adawa sun gaza kafa Gwamnati
Yunkurin Jam’iyyun adawar kasar Afirka ta kudu na kafa gwamanti a Jihohin da suka samu nasara bayan zaben da ya gabata yaci tura saboda bambacin ra’ayin dake tsakanin su.
Wallafawa ranar:
Shugaban Jam’iyyar EFF Julius Malema yace ba zasu shiga kawance da wata Jam’iyya ba amma zasu goyi bayan Jam’iyyar Democratic Alliance dan tababtar da cewar ANC bata kafa gwamnati ba.
Shima jagoran DA Mmusi Maimane ya tababtar da cewar babu yarjejeniya tsakanin su da wata jam’iyya ta dunkulewa.
Jam’iyyar ANC mai mulki ta fuskanci raguwar karbuwa ga jama’ar Afirka ta Kudu saboda zargin cin hanci da rashawa da ya dabaibaye gwamnatin kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu