Isa ga babban shafi
Afrika ta kudu-Najeriya

Afrika ta kudu ta fi Najeriya Karfin tattalin arziki

Afrika ta kudu ta koma matsayinta na kasa mafi girman tattalin arziki a Afrika, bayan doke Najeriya a ma'auni Arzikin kasa duk da matsalolin koma baya da ta ke fuskanta. 

Tattalin arzikin Najeriya ya fadi warwas
Tattalin arzikin Najeriya ya fadi warwas REUTERS/Afolabi Sotunde
Talla

Dukkannin kasashen biyu sun fuskanci koma bayan tattalin a cikin wannan shekarar. Sai dai yayin da Afrika ta Kudu ta samu tagomashi kan kudin kasar ta da 16 cikin 100 a bana, faduwar darajar Naira a Najeriya ya durkusar da ita sama da kashi 3 na yawan girman tattalin arzikin ta.

A cewar kafar yadda labaran Bloomberg, dake rawaito rahotanni IMF, ma’aunin tattalin arzikin Najeriya a yanzu na kan dala biliyan 296, na Afrika ta kudu kuma na kan dala biliyan 301.

Najeriya dake fuskantar barazanar tattalin arziki irinsa na farko cikin shekaru. A shekara ta 2014 kasar ta kasance kasa mafi girman tattalin arziki a Afrika lokacin da ma ‘aunin tattalin arzikinta ya zarce dala biliyan 500 irinsa na farko a shekaru 20.

A yanzu dai Afrika ta Kudu ta dawo matsayin da Najeriya ta kwace mata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.