Isa ga babban shafi
Afrika ta kudu

Jam’iyyar ANC mai mulkin Afrika ta Kudu ta koyi darasi

Jam’iyyar ANC mai mulkin Afrika ta Kudu ta ce, ta koyi darasi a zaben kananan hukumomi da aka gudanar, inda sakamakon zaben ke nuna cewa, al’ummar kasar sun dawo daga rakiyar jam’iyyar.

Shugaban kasar Afirka ta Kudu Jacob Zuma
Shugaban kasar Afirka ta Kudu Jacob Zuma REUTERS/Mike Hutchings
Talla

Jam’iyyar ANC wadda ta fara mulkin kasar tun shekara ta 1994, bayan kawo karshen mulkin wariyar launin fata ta fuskanci babban koma baya a wannan karon, batun dake nuna farin jinin ta na gab da disashewa.

Duk da dai jumullar sakamako na nuna cewa, jam’iyyar  na kan gaba, ta samu koma bayan da bata taba ganin irinsa ba cikin shekaru 22.

Al'ummar Afrika ta Kudu na cigaba da bayyana takaicinsu dangane da durkushewar tattalin arziki da rashin ayyukan dake cigaba da yi musu katutu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.