Isa ga babban shafi
Masar

‘Yan fashi sun karkatar da jirgin Masar zuwa Cyprus

‘Yan sandan Cyprus sun ce Jirgin EgyptAir na kasar Masar da wasu ‘yan fashi da ba a tantance ba suka karkatar ya sauka a filin jirgin Larnaca kudancin kasar a yau Talata. Yanzu haka an baza jami’an tsaro a filin jirgin.

Jirgin EgyptAir na Masar
Jirgin EgyptAir na Masar REUTERS/Mohamed Abd El Ghany/Files
Talla

Rahotanni sun ce wani dan bindiga ne guda ya kwace ikon jirgin mai dauke da fasinja kimanin 80 akan hanyarsu daga birnin Alexandria zuwa Al Kahira.

‘Yan sandan Cyprus sun ce Maharin ya nemi izinin sauka filin jirgin Larnaca da safiyar yau Talata. Zuwa yanzu babu wani cikakken bayani akan dalilin sace jirgin.

Rahotanni sun ce dan bindigar ya ba fasinjojin da ke cikin jirgin ficewa amma tare da yin garkuwa da wasu Turawa 5 bayan sun sauka a Larnaca.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.