Najeriya
Fashewar bututun mai ya hallaka mutane 3 a Najeriya
Mutane 3 sun mutu wasu da dama sun jikkata sakamakon fashewar wani bututun mai a yankin Naija Delta dake Najeriya.
Wallafawa ranar:
Talla
Rahotanni na cewa bututun man da ya fashe mallakin Kamfanin hakar mai na Eni na kasar Italiya ne, kuma ya fashe ne a daidai lokacin da ake kan yiwa bututun gyara.
Al’amarin ya auku ne a wani yanki mai suna Olugboboro dake jahar Bayelsa tun ranar lahadin da ta gabata sai dai kuma a jiya litinin aka iya gano gawarwakin mutanen ukun
Kawo yanzu dai babu bayani daga Kamfanin ko bangaren gwamnati kasar game da wannan al’amari.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu