Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Demokradiyar Congo

An sami tsohon mataimakin shugaban DRC da hannu a laifukan yaki

Kotun hukunta manyan laifukan yaki ta ICC a yau litinin ta sami tsohon mataimakin shugaban kasa a Jamhuriyar Demokradiyar Congo Jean-Pierre Bemba da laifin yin sakaci har soji suka sami damar yiwa mata fyade da kisa a Afrika ta Tsakiya

Jean-Pierre Bemba, tsohon shugaban Jamhuriyar Demokradiyar Kongo
Jean-Pierre Bemba, tsohon shugaban Jamhuriyar Demokradiyar Kongo REUTERS/JERRY LAMPEN/Pool
Talla

Alkalin kotun ICC Sylvia Steiner, a lokacin da yake yanke hukunci yace Bemba ya ki hukunta sojan kungiyarsa ta Movement for the Liberation of Congo, a lokacin da suke ayyukan asha a kasa makwabciyarsu.

Bemba dai ya tafaka kuskure  ganin yadda dakarun dake karkashin kungiyarsa  suka yi ta yiwa mata fyade da kuma kisan mutane na ba gaira ba dalili inji ICC ba tare da yayi kokarin hanasu ba.

Wannan dai shine karo na farko da kotun ta sami wani jami’in gwamnati babba da alhakin laifin sojan dake karkashinsa.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.