Isa ga babban shafi
MDD

MDD zata rage yawan dakarun wanzar da zaman lafiya a Cote D'Ivoire

Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya tsaida shawaran rage yawan sojan wanzar da zaman lafiya da ake dasu a kasar Cote D’Ivoire, inda ake fama da yakin basasa na tsawon shekaru 5 da suka gabata.

Dakarun wanzar da zaman lafiya a Côte d'Ivoire
Dakarun wanzar da zaman lafiya a Côte d'Ivoire REUTERS/Luc Gnago
Talla

Wakilan majalisar su 15 ne suka amince da rage yawan Dakarun, 4,000 daga cikin 5,437 tun daga watan jibi, na Maris.

Matakin na zuwa ne bayan kasar ta yi nasarar gudanar da zabe sahihi da ya sake baiwa Shugaban kasar Alassane Ouattara damar lashe zaben mulkin kasar na tsawon shekaru 5.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.