Isa ga babban shafi
Burkina Faso

Ana zaben shugaban kasa a Burkina

Al’ummar kasar Burkina Faso na gudanar da zaben shugaban kasa da na ‘Yan Majalisun dokoki a yau Lahadi inda ‘Yan takara 14 ke neman shugabancin kasar.

Mutane sun yi layi domin zaben shugaban kasa da na 'Yan Majalisu a Ouagadougou, Burkina Faso
Mutane sun yi layi domin zaben shugaban kasa da na 'Yan Majalisu a Ouagadougou, Burkina Faso REUTERS/Joe Penney
Talla

Da sanyin safiya misalin karfe 6 aka bude runfunar zabe inda al’ummar kasar Miliyan 5 ke da ‘yancin kada kuri’a a zaben da ake gani mafi muhimmaci a Burkina faso bayan boren da ya kawo karshen mulkin shekaru 27 na Blaise Compaore.

Mutane 14 ke takarar shugabancin kasa, yayin da wasu daruruwa ke takarar neman shiga majalisar dokokin kasar mai kujeru 127.

Ana sa ran kammala zaben da misalin karfe 6 na yamma. Hukumar zaben kasar tace zuwa Litinin zata fitar da sakamako.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.