Isa ga babban shafi
Saliyo

Saliyo ta rabu da cutar ebola

Ranar Asabar mai zuwa ne ake saran ayyana kasar Saliyo a matsayin wadda ta rabu da cutar ebola bayan an kwashe kwanaki 42 ba tare da samun wanda ya kamu da cutar ba.

Cutar ebola ta hallaka mutane da dama a Saliyo da Guinea da Liberia.
Cutar ebola ta hallaka mutane da dama a Saliyo da Guinea da Liberia. REUTERS/Daniel Berehulak/The New York Times/
Talla

Sai dai har yanzu al’ummar kasar wadda ta rasa mutane sama 4,000 na ci gaba da zaman dar dar ganin yadda cutar ke ci gaba da hallaka mutane a kasar Guinea da ke makwabtaka da ita.

Palo Conteh, shugaban kai dauki kan masu fama da cutar a Saliyo ya ce babu wani biki da za a yi ranar  a Asabar, sai dai kawai farin cikin cewar sun rabu da cutar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.