Boko Haram ta kashe mutane uku a Abadam kudancin Nijar
Wasu da ake hasashen Mayakan kungiyar Boko Haram ne sun kai hari a kusa da garin Abadan da ke kan iyakar kasar Jamhuriyyar Nijar da Najeriya inda suka kashe mutane uku cikinsu har da sojan kasar daya.
Wallafawa ranar:
Kamfanin dillancin labarai Reuters ya ruwaito wata wata majiyar sojan Nijar ta tabbatar da cewa an hallaka ilahirin ‘yan ta’addar da suka kai harin a yankin Jihar Diffa kudancin Nijar.
Yankin Diffa dai na fama da matsalar ‘Yan Boko Haram. Kuma kimanin ‘Yan gudun hijira 150,000 suka tsallaka yankin daga Najeriya saboda rikicin Boko Haram.
Yanzu haka dai yankin Diffa na cikin dokar ta-baci.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu