Isa ga babban shafi
Burundi

Nkurunziza ya lashe zaben Kasar Burundi

Hukumar Zaben kasar Burundi ta bayyana shugaba mai ci Pierre Nkurunziza a matsayin wanda ya lashe zaben shugabancin kasar daka aka yi ranar Talata da ta gabata.

Shugaba Pierre Nkurunziza na Burundi
Shugaba Pierre Nkurunziza na Burundi AFP PHOTO / MARCO LONGARI
Talla

Hukumar zaben ta ce Nkurunziza ya samu fiye da kashi 69 cikin 100 na kuri’un da aka kada, kuma wannan ya bashi nasara a zaben, ba tare da bukatar zuwa zagaye na biyu ba.

Tuni jam’iyyun adawar kasar, dama manyan kasashen duniya, suka sa kafa suka yi fatali da zaben, da suka bayyana da cewa haramtacce ne, da bai da sahihanci.

Burundi ta tsinci kanta a halin rikici tun bayan da Nkurunziza ya bayyana aniyarsa ta neman shugabancin kasar a wa’adi na uku yayin da ‘yan adawa suka bayyana cewa kasar zata shiga mawuyacin hali fiye da wanda take ciki matukar Nkurunziza ya lashe zaben.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.