Mali
Mayakan Jihadi sun kashe Sojin mali
A kasar Mali, sojoji uku ne suka rasa rayukansu a wani hari da mayakan jihadi suka kaddamar a garin Nara dake kudu maso yammacin Kasar kuma ke kan iyaka da Kasar Mauritania.
Wallafawa ranar:
Talla
A wata sanarwa da gwamanatin Kasar ta fitar, ta bayyana bakin cikin mutuwar jami’a sojinta kuma ta kara da cewa , dakarunta sun yi nasarar hallaka mutane 9 daga cikin mayakan jihadin bayan sun mayar da martani.
Wata majiyar ta bayyana cewa an samu miyagun kwayoyi a cikin aljihun daya daga cikin mayakan jihadin da aka kashe.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu