Isa ga babban shafi
Faransa

Faransa za ta kara yawan tallafin rundunar MDD a Mali

Gwamnatin Kasar Faransa za ta kara yawan tallafin da take bai wa rundunar wanzar da zaman lafiya na Majalisr Dinkin Duniya a Kasar Mali. 

Ministan tsaron Faransa, Jean-Yves Le Drian tare da shugaban Kasar Mali Ibrahim Boubacar Keïta
Ministan tsaron Faransa, Jean-Yves Le Drian tare da shugaban Kasar Mali Ibrahim Boubacar Keïta AFP PHOTO / HABIBOU KOUYATE
Talla

Ministan tsaron Faransa ne Jean-Yves Le Drian ya bayyana haka a lokacin da yake gabatar da jawabi a garin Gao na arewacin kasar Mali.

A karshen wannan wata ne dai wa’adin aikin rundunar ta Majilisar Dinkin Duniya zai kawo karshe, amma ana fatar kwamitin tsaro na majalisar zai tsawaita wa’adin aikin rundunar, yayin da sojojin Faransa da ke aiki a kasar za su danka wa rundunar wasu daga cikin yankuna da ke karkashin kulawarsu a arewacin Mali bayan sulhun da aka cimma tsakanin gwmanati da ‘Yan tawaye.

Kasar Faransa nada dakaru kimanin 1, 350 da ta aike a matsayin gudun mawarta danagane da yaki da ta'addaci a Mali.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.