Liberia ta rabu da Ebola-WHO
A yau assabar Hukumar Lafiya ta duniya WHO, ta tabbatar da cewa babu sauran cutar Ebola a Liberia, bayan daukan tsahon kawanaki 42 ana sa’ido ba tare da an samu wani wanda ya kamu da cutar ba.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Sai dai WHO ta gargadi cewa kar a sakankance domin har yanzu akwai sauran cutar a makwabtan kasar ta Liberia, wato Guinea da Saliyo.
Shugabar Liberiar Ellen Johnson Sirleaf ta bayyana farin ciki ta akan wannan nasara
Fiye da shekara guda da ta wuce ne kasar ta Liberia ta ba da rahoton kamuwa da cutar a karo na farko bayan cutar ta yadu daga Guinea.
Tuni kasar Amurka ta aikawa Liberia sakon taya murna akan wannan cigaba da aka samu
Cutar ebola dai tayi ajali mutane sama da dubu 4 a liberia
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu