An cafke mutane da dama kan zargin juyin mulki a Gambia
An cafke mutane da dama, da ake zargi suna da hannu a yunkurin jurin juyin mulkin da aka yi a kasar Gambia, lokacin da shugaban kasa Yahya Jammeh ke ziyara a birnin Dubai, wanda kuma ya dora alhakin harin kan ‘yan kasashen waje da bai bayyana sunayen su ba.
Wallafawa ranar:
Wata majiya daga bangaren leken asirin kasar, tace an kuma sami makamai masu tarin yawa da abubuwa masu fashewa, da aka so yin amfani dasu a yunkurin juyin mulkin, na daren ranar Talata.
Yanzu haka dai ana tsare da wadanda ake zargi da hannu a lamarin, a wasu gidajen da ke Banjul fadar gwamnatin kasar.
Yahya Jammeh ya kwashe shekaru 20 yana shugabanci a Gambia, kuma ya zargi kasashen waje da ke adawa da gwamnatinsa da ke son kawo karshen mulkinsa a Gambia
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu