Isa ga babban shafi
Gambia

Amurka ta la’anci yunkurin juyin mulki a Gambia

Gwamnatin kasar Amurka ta yi Allah wadai da yunkurin juyin mulki a kasar Gambia tare da yin kira ga Amurkawa su kauracewa babban birnin kasar har sai an samu kwanciyar hankali. Amurka ta kuma yi kira ga bangarorin Gambia su kujewa rikici a cikin kasar.

Kofar shiga Banjul, babban birnin kasar Gambia
Kofar shiga Banjul, babban birnin kasar Gambia Wikimedia
Talla

Ofishin jekadancin Amurka a Gambia ya fadi a cikin wata sanarwa cewa zai ci gaba da lura da halin da ake ciki a kasar tare da yin kira ga Amurkawa su kauracewa babban birnin kasar Banjul.

A ranar Talata ne aka yi kokarin murkushe wani yunkurin juyin mulki da wasu gungun Sojojin Gambia suka so kifar da gwamnatin Yahya Jammeh wanda ke ziyara a Dubai.

Rahotanni daga Gambia sun ce an cafke mutane uku da ake zargi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.