Isa ga babban shafi
Najeriya

Adamu Mu’azu ne sabon shugaban Jam'iyyar PDP a Najeriya

Kwamitin Zartarwar Jam’iyyar PDP mai mulki a Najeriya ya tabbatar da Tsohon Gwamnan Jahar Bauchi Adamu Mu’azu a matsayin sabon shugaban Jam’iyyar kafin a gudanar da zabe bayan murabus din Alhaji Bamanga Tukur. Tuni dai aka rantsar da Mu’azu kuma Gwamnan Bauchi ne na yanzu Malam Isa yuguda ya mika sunan shi.

Tsohon Gwamnan Bauchi Adamu Mu'azu sabon shugaban Jam'iyyar PDP mai mulki a Najeriya
Tsohon Gwamnan Bauchi Adamu Mu'azu sabon shugaban Jam'iyyar PDP mai mulki a Najeriya manroviapost
Talla

A dokar Jam’iyyar PDP, kwamitin Zartarwa yana da ikon zaben shugaban riko don maye gurbin shugaban da ya yi murabus.

Mu’azu, Tsohon gwamnan Bauchi ne har sau biyu a 1999 da 2007, ya fuskanci suka a lokacin da Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ya nada shi shugaban hukumar Fansho. Daga Abuja Aminu Manu ya aiko da Rahoto.

01:29

Rahoto: Adamu Mu’azu ne sabon shugaban Jam'iyyar PDP

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.