Mali
Al'ummar Mali suna dakun sakamakon zaben shugaban kasa
Al’ummar kasar Mali sun jiran sakamakon zaben shugaban kasa da aka gudanar karo na farko tun da sojoji suka yi juyin mulki, kasashen duniya sun yaba da yadda aka gudanar da zaben da kuma yadda mutane suka fito domin kada kudir’a amma Rahotanni daga kasar Mali na nuni da cewa ga dukkanin alamu sai an je zagaye na biyu na zabe kafin a samar wa kasar da sabon shugaba, yayin da jami’an hukumar zabe ke ci gaba da tattara sakamakon zaben zagayen farko da aka gudanar a ranar lahadin da ta gabata. Salissou Hamissou ya aiko da rahoto daga birnin Bamako.
Wallafawa ranar:
Kunna - 01:35