Isa ga babban shafi
Mali

Shugabannin Afrika ta Yamma sun nemi taimakon Dala miliyan 25 domin gudanar da zaben Mali

Shugabannin Kasashen Afrika ta yamma, sun bukaci kasashen duniya da su taimaka musu da tsabar kudi Dala miliyan 25 dan gudanar da zaben kasar Mali da aka shirya yi a karshen wannan wata.

Daga Hagu Shugaban kasar Nijar Mahamadou Issoufou, Shugaban kasar Burkina Faso  Blaise Compaore, Shugaban kasar Ivory Coast  Alassane Ouattara da shugaban kasar Benin Thomas Boni Yayi a wani Taron kasashen kungiyar ECOWAS
Daga Hagu Shugaban kasar Nijar Mahamadou Issoufou, Shugaban kasar Burkina Faso Blaise Compaore, Shugaban kasar Ivory Coast Alassane Ouattara da shugaban kasar Benin Thomas Boni Yayi a wani Taron kasashen kungiyar ECOWAS REUTERS/Thierry Gouegnon
Talla

Shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan da takwaransa na Cote d’Ivoire, Alassane Ouattara ne suka bayyana haka, a taron da suki yi a Abuja.

Wannan kira na zuwa ne a dai dai lokacin da ake shirin kammala taron shugabanin kasashen Afrika ta Yamma a yau, inda suke nazari kan yadda za’a gudanar da karbabben zabe a kasar ta Mali, ba tare da samun tashin hankali ba.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.