Isa ga babban shafi
Mali

Sojin Mali sun shiga garin Kidal yayin da aka fara yakin neman zabe a kasar

Yanzu haka sojojin kasar Mali sun yi nasarar shiga garin Kidal dake hannun ‘Yan tawaye, yayin da ake cigaba da shirin zaben shugaban kasa a karshen wannan wata.

Daya daga cikin 'yan takarar shugaban kasa a Mali, Ibrahim Boubakar Keita
Daya daga cikin 'yan takarar shugaban kasa a Mali, Ibrahim Boubakar Keita AFP PHOTO / HABIBOU KOUYATE
Talla

Rahotanni sun ce ‘Yan takara 24 sun fara yakin neman zabe, wanda za a gudanar a ranar 28 ga wannan wata na Yuli.

Wannan zabe shine na farko tun bayan hambarar da gwamnatin kasar a watan Maris din shekarar da ta gabata.

Wasu da dama dai na ganin an saka hanzari a gudanar da zaben kasar yayin da wasu ke ganin cewa lokacin ya yi da za a mayar da kasar kan turbara demokradiya.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.