Isa ga babban shafi
Nijar

Mayakan MUJAO na Mali sun yi ikirarin daukar alhakin kai harin Agadez

Mayakan kungiyar MUJAO masu neman tabbatar da Shari’ar Musulunci a kasar Mali sun yi ikirarin daukar alhakin kai harin da ya kashe mutane kimanin 19 a sansanin Soji da kuma kamfanin Uranium na Faransa a kasar Jamhuriyyar Nijar.

Mayakan Kungiyar MUJAO a Mali
Mayakan Kungiyar MUJAO a Mali Adama Diarra /Reuters
Talla

“Mun gode Allah, mun kai jerin hare hare guda biyu ga makiyan Addinin Islama a Nijar” a cewar Kakakin kungiyar Abu Walid Sahraoui.

Abu Walid ya shaidawa kamfanin Dillacin Labaran Faransa cewa sun kai harin ne domin mayar wa Nijar da martani game da hadin kan da ta ba Faransa domin yaki da shari’ar Allah a Mali.

Ministan cikin gidan Nijar Abdou Labo ya tabbatar da mutuwar mutane 19 a hare haren da aka kai a Jahar Agadez da suka hada da dakarun Soji 18 da wani farar hula.

Wannan harin dai shi ne na farko da aka kai a Nijar da ke Makwabtaka da Mali. Kuma Nijar ta taimaka da Dakarunta zuwa Mali domin kakkabe ‘yan tawaye da suka karbe ikon Arewacin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.