Najeriya
An saki jirgin ruwan da ‘Yan Fashi suka sace da Turawa a Bayelsa
‘Yan fashin jiragen ruwa a Najeriya, sun saki matuka wani jirgin ruwa shida da suka sace a Jihar Bayelsa, kwanaki tara ta suka gabata. Mutanen sun hada da Yan kasar Ukraine uku da Dan Rasha guda da ‘Yan kasar India uku. Yankin Niger Delta na daya daga cikin Yankunna da ke fama da matsalar tsaro, wanda ke shafar aiyukan kamfanonin mai, kamar yadda kanfanin Exxon Mobil da Shell suka bayyana a makon jiya.
Wallafawa ranar: