Boko Haram ta dauki alhakin kai hare hare kan cibiyoyin sadarwa a Najeriya
Kungiyar Jama’atul Ahlis Sunnah Lid da’awati wal Jihad da ake kira da suna Boko Haram ta yi ikirarin daukar alhakin kai hare hare a cibiyoyin wayoyin sadarwa a arewacin Najeriya, tare da gargadin kai wa ‘Yan Jaridu da Muryar Amurka hari.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Tsakanin Talata da Laraba ne aka kai wasu jerin jerin hare a cibiyoyin wayoyin sadarwa a Bauchi da Gombe da Yobe da Kano.
A wani sakon email da kungiyar ta yada, kakakinta Abul Qaqa, ya ce sun dauki matakin kai wa cibiyoyin hari ne sakamakon hadin kai da suke ba jami’an tsaro domin cafke mambobinsu.
Yanzu haka kuma Kamfanonin sadarwa na wayoyin salula, mtn da airtel da glo etisalat sun yi gargadin ficewa daga yankin arewacin kasar, domin hasarar da kudi da aka janyo masu ta kusan sama da naira biyan daya
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu