Tsohon Shugaban Najeriya Obasanjo ya isa kasar Senegal domin shiga tsakani
Tsohon Shugaban Nigeria Olusegun Obasanjo ya sauka a Darkar babban birnin kasar Senegal, domin fara aikin da aka bashi na shiga tsakani a rikicin kasar a madadin kungiyar kasashen Yammacin Afrika dama kungiyar kasashen Tarayyar Africa.
Wallafawa ranar:
Olusegun Obasanjo zai sa idanu a zaben da za ayi ranar Lahadi inda Shugaba maici Abdullah Wade, dan shekaru 85 da haihuwa, ke neman zarcewa da mulkin kasar wa'adi na uku, wanda ya janyo tayar da jijiyoyin wuya tsakaninsa da 'yan adawa. Lamarin da ya haifar da bore tare da tashin hankalin siyasa.
Ya zuwa yanzu dai mutane akalla shida suka rasa rayukansu, kuma masu kyamar tazarcen na cewa a fito a bijirewa tazarcen.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu