Libya zata tura ‘Yantawaye horon soji zuwa Jordan
Kasar Libya tace zata tura tsofaffin ‘yan tawayen da suka yaki tsohon shugaban kasar Kanal Ghaddafi, su dubu 10 zuwa kasar Jordan don samun horon da zai taimaka a shigar da su aikin Soji a kasar.A cewar kakakin ma’aikatar cikin gidan kasar, Janar Abdelmonem al-Tunsi, akwai yarjejeniya da kasar Libya ta kulla da kasar Jordan domin bayar da horo ga ‘yan kasar 10,000.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Wata Takardar yarjejeniyar da kamfanin Dillacin Labaran AFP ya samu, an bayyana cewa a farkon watan Mayu ne ‘Yantawayen kimanin 1,000 zasu fara karbar horo a Jordan kafin tura wasu 2,000.
Mista Tunsi yace sun yanke shawarar kulla kawance da Jordan ne saboda kwarewarta wajen aikin horar da ‘Yan sandan kasar Iraqi.
Yanzu haka kuma ma’aikatar cikin gidan ta fara karbar takardun makarantar ‘Yantawayen domin samun shiga shirin horon aikin soji.
‘Yantawayen dai sune suka kwashe watanni suna yaki da dakarun Kanal Ghaddafi tare da samar da tsaro a kasar Libya kafin kashe Ghaddafi a Octoban bara.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu