Dakarun kudancin Sudan sun kai hari Uganda
Dakarun sojin kudancin Sudan sun kai wani hari cikin kasar Uganda tare da garkuwa da mutane 15 da suka hada da mata, wadanda kungiyar SPLA ta zarga da shiga cikin Sudan suna dibar amfanin gona, abunda ke kara cusa tsoro kan iyakar kasashen biyu.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Sai dai kuma Ministan yada labaran Uganda, Kabakunbo Musiko, ta bayyana cewa yankin yana cikin kasar ta Uganda ne.
Dangane da taswirar da ake amfani da shi, wannan yankin yana cikin kasar Uganda, bayan yankin da babu mai mallaka tsakanin Uganda da Sudan. Kasar Sudan ta san wannan yankin na Uganda ne, amma ba’a cimma yarjejeniya ta karshe ba, kuma karkara zasu iya gaba gadi ba tare da sanin gwamnati ba.
Kalaman Ministar Uganda
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu