Korea ta Arewa ta lalata cibiyar gwajin nukiliyarta
Korea ta Arewa ta lalata cibiya daya tilo ta gwajin makamin nukiliyarta, a wani mataki na kokarin sassauta tashin hankali a yankin.
Wallafawa ranar:
‘Yan jaridun kasashen duniya da suka halarci cibiyar gwajin nukiliyar ta Punggye-ri da ke yankin arewa maso gabashin kasar, sun ce sun shaida wata gagarumar fashewa a yayin gudanar da aikin lalatawar.
Mahukuntan Korea ta Arewa sun sanar da aniyarsu ta da lalata cibiyar a farkon wannan shekarar, a wani mataki na farfado da kyakkyawar dangantakar diflomasiya tsakanin kasar da makwabciyarta Korea ta Kudu da kuma Amurka.
Sai dai masa kimiya na ganin cewa, tun a cikin watan Satumban bara ne wani sashi na cibiyar ya ruguje bayan wani gwaji da kasar ta gudanar, abin da masana kimiyar ke ganin cewa, tuni cibiyar ta rasa karsashi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu