Isa ga babban shafi
Hague-Lebanon

An bude sauraren karar kisan Hariri na Lebanon

An bude shari’ar mutane hudu da ake zargi sun kashe Firaministan kasar Lebanon Rafiq Hariri a shekarar 2005 amma ba a gaban idon mutanen ba wadanda ake zargi kuma mayakan kungiyar Hezbollah ne.

Hoton Tsohon Firaministan kasar Lebanon Rafic Hariri wanda harin bam ya kashe a birnin Beirut a 2005
Hoton Tsohon Firaministan kasar Lebanon Rafic Hariri wanda harin bam ya kashe a birnin Beirut a 2005 AFP PHOTO/JOSEPH EID
Talla

An kashe Hariri ne tare da wasu mutane sama da 20 a wani harin bam da aka kai a birnin Beirut a shekarar 2005 wanda ya raunata mutane 225.

An bude sauraren karar mutanen ne hudu da ake zargi wadanda har yanzu ba a cafke ba a kotun hukunta laifukan yaki a birnin Hague.

Tuni dai kungiyar Hezbollah ta nisanta kanta da daukar alhakin kai harin amma tace kisan Hariri minakisa ce tsakanin Isra’ila da Amurka.

A shekarar 2011 ne kotun Hague ta bayar da sammacin kamo mutanen hudu da ake zargi wadanda aka bayyana sunayensu a matsayin Mustafa Badreddine da Salim Ayyash da Hussein Oneissi da Assad Sabra dukkaninsu mambobin kungiyar Hezbollah ta mabiya Shi’a.

A ranar Masoya ne aka kashe Firaminista Hariri Dan Sunni.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.