Faransa na fatan Amurka ta ci gaba da kasancewa Sahel
A gobe litinin ake sa ran Ministan tsaron Faransa Florence Parly za ta ziyarci cibiyar tsaron Amurka Pentagon a birnin Washington don tattauna da hukumomin dangane da goyan bayan Amurka a yakin da sojan ta ke yi a yankin Sahel.
Wallafawa ranar:
Ministar tsaron Faransa Florence Parly za ta yi amfani da wannan dama domin shawo kan hukumomin Amurka na ganin Amurka ta ci gaba da kasancewa a yankin Sahel tareda kawo goyan bayan don kawar da mayakan jihadi a Sahel.
Zuwan Florence Parly Amurka a gobe na zuwa ne bayan da daya babban hafsan sojan Amurka Janar Mark Milley ya bayyana cewa Amurka na nazarin rage adaddin sojan ta daga Afrika..
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu