Isa ga babban shafi
Turai

Turai ta yi barazanar hana Visa ga kasashen afrika da suka ki bata hadin kai ta magance matsalar yan ci rani.

Kungiyar tarayyar turai ta yi barazanar hana wasu kasashen Afrika Visa shiga nahiyar, matsawar suka ki bada hadin kai, wajen kwashe bakin haure yan kasashen su da suka shiga turai ta barauniyar hanya su mayar dasu kasashensu.

komishinan kaurar jama'a na kungiyar tarayyar turai  Dimitris Avramopoulos. Bruxelles,  27 mayu 2015
komishinan kaurar jama'a na kungiyar tarayyar turai Dimitris Avramopoulos. Bruxelles, 27 mayu 2015 REUTERS/Francois Lenoir
Talla

Kungiyar ta tarayyar turai na bukatar ganin ta samu hadin kan kasashen na Afrika ne wajen kwashe bakin hauren yan kasashensu domin magance matsalar da ta dada yin muni a 2015 matsalar bakin hauren da ake ganin ita ce irin mafi muni da nahiyar Turai ta gani tun bayan yakin duniya na 2.

A lokacin da yake jawabi a Bruxell Komishinan dake kula da kaurar jama’a na tarayyar turai Dimitris Avramopoulos ya ce, ya yi matukar mamaki a cewa kasashen kasashe ne dake da kyaukyawar hulda da turai amma su ki bada hadin kai wajen sake mayar da yan kasashensu gida dake saune a turai ba tare da takardun izinin zama ba.

Ya kara da cewa daga yanzu kungiyar zata gindaya sharadin kin bada visa ga duk wata kasa abikiyar hulda da taki amincewa ta kwashe yan kasarta da suka shiga kasashen na turai ta barauniyar hanaya.

A karkashin dokokin duniya ko na turai dai, babu inda aka ce kasashen turai su baiwa da baki yan ci rani matsugunni a cikin kasashensu, amma dokokin sun bukaci su karbi yan gudun hijirar dake tserewa yaki a kasashen da suka baro

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.