Isa ga babban shafi
Afirka

Shugabannin Afirka na son lalubo hanyar tabbatar da tsaro

Shugabannin ƙasashen Afirka da ke halartar taron A.U a Addis Ababa sun gudanar da wata tattaunawa kan samar da zaman lafiya da tsaro a faɗin nahiyar.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da shugaban Ivory coast Alassane Ouattara.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da shugaban Ivory coast Alassane Ouattara. REUTERS/Luc Gnago
Talla

Shugabannin sun tattauna a kan rikice-rikice da suka ƙi ci suka ki cinyewa a wasu yankuna, da matsalar ƴan gudun hijira, da kuma matsalar sauyin yanayi.

A lokacin zaman an zanta kan rikicin Somalia da Libya, da Jamhuriyar Afirka ta tsakiya, da yankin tafkin Chadi da wasu yankunan da dama.

A ranar lahadi ne ake za a bude babban taron, yayin da a ranar Litini shugaban Nigeria Muhammadu Buhari zai ƙaddamar da sabon tambarin yaƙi da rashawa na ƙungiyar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.