Afrika ta Tsakiya na fuskantar rashin Tsaro
Kungiyoyin Agaji sun bukaci Majalisar Dinkin Duniya da ta dauki matakin gaggawa kan halin kunci da mutanen Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya ke ciki ganin yadda tashin hankali ya daidaita kasar.
Wallafawa ranar:
Wata wasika da kungiyoyin suka rubutawa Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres, kungiyoyin sun bayyana damuwar su kan yadda harkar tsaro ke ci gaba da tabarbarewa.
Wasikar hadin kan tace fararen hula 821 suka rasa rayukan su, inda ta bukaci Sakatare Janar Guterres da yayi amfani da ofishin sa wajen kawo karshen wannan rikici dake ci gaba da tsananta.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu