Zulum ya ziyarci 'yan gudun hijirar Boko Haram a Nijar
Gwamnan Jahar Borno Farfesa Baba Gana Umara Zulum, ya ziyarci ‘yan gudun hijarar jihar sa da suka tserewa rikicin Boko Haram zuwa jamhuriyar Nijar.
Wallafawa ranar:
Zulum tare da rakiyar wasu mukarraban gwamnatinsa da wasu ‘yan Majalisun dokokin jahar ciki harda shugaban Majalisar, ya rarraba kayayyakin agaji ga ‘yan gudun Najeriya dake sansanin ‘yan gudun hijirar jamhuriyar Nijar.
Kwanakin baya ma gwamna Zulum ya kai ziyara daya daga cikin manyan sansanonin ‘yan gudun hijarar Najeriya a kasashen Makwabta, wato Minawawo na kasar Kamaru dake da ‘yan gudun hijirar Najeriya da suka kauracewa rikicin Boko Haram sama da dubu 40.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu