Isa ga babban shafi
Najeriya

Wamakko da Bafarawa sun yi cacar-baka gaba da gaba

Tsoffin gwamnonin jihar Sokoto, Attahiru Dalhatu Bafarawa da Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko sun yi yakin cacar-baka gaba da gaba a filin jiragen sama na Sultan Abubakar na uku da ke jihar.

Wamakko da Bafarawa
Wamakko da Bafarawa Facebook
Talla

Rahotanni sun ce, Bafarawa ya fusata biyo bayan kalaman da Wamakko ya furta, inda yake bayyana Bafarawan a matsayin dan ci-rani a jihar.

Wannan ne ya sa Bafarawan ya ki amsa gaisuwar da Wamakko ya yi masa a yayin da suka hadu a filin jirgin saman a ranar Litinin.

A maimakon amsa gaisuwar, Bafarawa ya fada wa Wamakko cewa, “ ka ce, ni dan ci-rani ne a Sokoto, me ya sa kake gaishe ni? Na san cewa, an haifi mahaifina da kakana a nan kuma sun mutu a nan. Zan iya nuna maka kaburburansu. Za ka iya nuna min kabarin kakanka? “

Sai dai Wamakko ya ki mayar masa da martani, amma ya tsaya kan bakarsa cewa, Bafarawa dan ci-rani ne.

A cewar wamakko, “ ba na bukatar sanin inda aka binne mahaifinka da kakanka, abin da na sani shi ne, kai dan ci-rani ne a Sokoto..

Kodayake tsoffin gwamnonin biyu sun shiga jirgi guda zuwa birnin Abuja.

Wamakko dai ya yi wa Bafarawa mataimakin gwamna har kusan shekaru 8 kafin daga bisani ya yi murabus don kashin kansa domin kauce wa tsigewa.

Wamakko ya gaji Bafarawa a kujerar gwamna bayan ya yi nasarar doke Alhaji Muhammadu Mai Gari Dingyadi, dan takarar da Bafarawa ya mara wa baya a zaben 2007.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.