Isa ga babban shafi
Najeriya

Buhari ya nada sabbin mataimaka 11

Jim kadan bayan tabbatar Boss Mustapha a matsayin sakataren gwamnatin Najeriya, da kuma Abba Kyari kan mukaminsa na shugaban ma’aikatan fadar gwamnati, shugaban kasar Muhammadu Buhari, ya sake nada Karin wasu hadiman fadar gwamnatinsa.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari. AFP/SAUL LOEB
Talla

Karin Jami’ai 11 fadar shugaban kasar ta sanar da nadawa a wannan Juma’a.

Daga cikin sabbin jami’an kuma akwai, Ya’u Shehu Darazau, mataimakin shugaban kasakan ayyuka na musamman, Muhammad Sarki Abba, a matsayin mataimakin shugaban kasa kan gudanar da harkokin yau da kullum a fadar gwamnati, sai kuma Dr Suhayb Rafindadi a matsayin likitan shugaban kasa.

Nadin mukaman, ya zo ne a daidai lokacin da ‘yan Najeriya suka kosa bisa jiran ganin wadanda za su bayyana a matsayin mukarraban sabuwar gwamnatin kasar da ta yi tazarce, bayan sake lashe zaben shugaban kasa da ta yi, a watan Fabarairu na 2019 da muke ciki.

Sanarwar kakakin shugaban Najeriyar malam Garba Shehu, ta ce nadin mukaman ya soma aiki ne, daga ranar 29 ga watan Mayu da ya gabata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.