Macron ya dai yi tir da matakin Gwamnatin sojin Mali (France 24- Rfi)
Kwana daya biyo bayan matakin gwamnatin sojin Mali na hana kafafen yada labaren Faransa da suka hada da tashar tashar talabijen France 24 da gidan rediyon Faransa na RFI yada shirye-shiryensu cikin kasar,Shugaban Faransa Emmanuel macron ya soki wannan mataki.
Wallafawa ranar:
Kunna - 00:39
Shugaban Faransa Emmanuel Macron na Allah wadai da kakkausar murya kan wannan mataki da ya sabawa kimar da al'ummar Mali da kasar ke tafiya a kai tun bayan samun 'yancin kai.
"kazzalika a jiya alhamis, hukumar gudanawar ta kafafen yada labaran Faransa da ke yada shirye-shriye zuwa kasashen ketare ta yi tir da dangane da yunkurin gwamnatin mulkin sojin Mali na hana tashar talabijin ta France 24 da kuma RFI yada shirye-shiryensu a cikin kasar.
Sanarwar da ta fitrar a jiya alhamis, hukumar gudanarwar ta ce za ta yi amfani da dukannin hanyoyi na doka, domin kalubalantar wannan mataki.
Ga abinda shugaban na Faransa Emmanuel Macron ke cewa jim kadan da samun labarin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu