Isa ga babban shafi

Yan ta’adda sun saki wasu ‘Yan kasar China guda biyu a Sahel

Rahotanni daga Burkina Faso sun ce Yan ta’adda sun saki wasu ‘Yan kasar China guda biyu dake aikin hakar ma’adinai bayan kwashe watanni 9 da garkuwa da su.

Sojojin kasar Burkina Faso.
Sojojin kasar Burkina Faso. © REUTERS/Luc Gnago
Talla

Hukumomin tsaron Jamhuriyar Nijar sun shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa sakin mutanen biyu wadanda aka sace a Nijar.

Yankin tafkin Chadi.
Yankin tafkin Chadi. AFP - JEREMY MAROT

Jakadan China a Yammai Jiang Feng ya yabawa gwamnatin Nijar akan rawar da ta taka wajen ganin an saki mutanen, inda ya bayyana matakin a matsayin nasarar da hukumomin Nijar ke samu wajen yaki da ta’addanci.

Feng ya bayyana haka ne bayan ganawar da yayi da shugaban kasa Bazoum Mohammed.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.