Isa ga babban shafi
Majalisar Dinkin Duniya

An nemi MDD ta gindaya 2030 a matsayin shekarar da za a kawo karshen talauci a duniya

Shugabannin kasashen Indonesia, Liberia da kuma Firaministan Birtaniya, sun bukaci Majalisar Dinkin Duniya da ta ayyana shekara ta 2030 idan Allah ya kai mu a matsayin shekarar da za a kawo karshen talauci a duniya baki daya.

Janar Sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Ban Ki-moon
Janar Sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Ban Ki-moon
Talla

Shugaban Indonesia Susilo Bambang, da shugaban Liberia Ellen Johnson Sirleaf da kuma Firaministan Birtaniya David Cameron, sun bayyana cewa akwai bukatar Majalisar ta samar da wani shiri da zai kawo karshen talauci da kuma samar da daidaito a tsakanin al’ummar duniya kafin shekarar ta 2030.

A daidai lokacin da Shirin Cimma Muradun Karni na MDD ya dogara a kan batutuwan da suka shafi kiwon lafiya da kuma yaki da talauci.

Shugabannin kasashen uku sun ce akwai bukatar Majalisar ta sanya batun rikice-rikice, da yake-yaken basasa, samar da kyakkyawan jagoranci da kuma yaki da rashawa a matsayin manyan ginshikai da za su kai ga samar da nasarar cimma wani buri.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.