Isa ga babban shafi
Majalisar Dinkin Duniya

Ban ki-moon ya nuna damuwarsa da shigar Hizbullah rikicin Syria

Janar Sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Ban ki-moon, ya nuna matukar damuwarsa kan shigar kungiyar Hizbulla cikin rikicin Syria. 

Shugaban Majalisar Dinkin Duniya, Ban Ki-moon
Shugaban Majalisar Dinkin Duniya, Ban Ki-moon REUTERS/Michael Kooren
Talla

A wata sanarwa da majalisar ta fitar sa’oi kadan bayan rokoki biyu da aka harba kan yankin kungiyar ta Hizbullah Ban ya yi kira ga daukacin kungiyoyi da kasashe da su kaucewa ruruta rikincin kasar ta Syria.

“Janar Sakataren Majalisar Dinkin Duniya ya cike da damuwa game da yadda rikicin ke kara tsananta.” Kamar yadda sanarwar ta nuna.

Ana zargin kungiyar ta Hizbulla wacce ke da tushe daga kasar Lebanon da taimakawa bangaren Shugaba Bashr al - Assad wajen samun nasara a kokarin da bangarorin biyu ke yi na mallake garin Qusayr, wanda ke kusa da kan iyakar kasar ta Lebanon.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.