Isa ga babban shafi
Najeriya

Kotu ta yankewa Henry Okah hukuncin daurin shekaru 24

Wata kotu a kasar Afrika ta Kudu ta yanke wa Henry Okah, hukuncin zaman gidan yari na tsawon shekaru 24, mutumin da ake zargi da kai harin bam a Abuja babban birnin Tarayyar Najeriya a shekarar 2010. An yanke wa Okah hukuncin bayan kotun ta same shi da laifuka 13 da suka hada da ayyukan ta’addancin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane 12 a harin bam din na Abuja.  

Talla

“A dalilin haka ne, aka yankewa Okah hukuncin zaman gidan yari na tsawon shekaru 24.” Inji Alkali Neels Claassen.

Mutane 12 ne suka rasa rayukansu a lokacin da bama-baman suka tashi, a dai dai lokacin da ake bikin cika shekaru 50 da samun ‘yanci kai a Najeriya.

A lokacin karar an yi zargin cewa, Okah bai nuna cikakkiyar nadama ba akan abin da ya aikata, domin a cewar rahotanni, ainihin nufinsa shi ne a samu hasarar rayuka da dama kamar yadda rahotanni suka nuna.

Kungiyar fafutuka ta neman ‘yancin yankin Niger Delta da aka fi sani da MEND a takaice wacce Okah ya ke jagoranta, ta dauki alhakin harin a lokacin, sai dai Okah wanda mazauni ne a kasar ta Afrika ta Kudu na dindindin, ya musanta zargin cewa yana da hanun a harin, inda ya ce an alakanta shi da harin ne saboda siyasa.

Har ila yau kotun ta same shi da laifin saka hanu a wasu hare-hare da aka kai guda biyu a garin Warri da ke kudancin Najeriya.

 

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.