Isa ga babban shafi
Najeriya

Chinua Achebe, marubuci a Najeriya ya mutu

Shahararren marubucin Najeriya Chinua Achebe, masanin adabi ya mutu yana shekaru 82. Chinua Achebe, ya yi suna a Afrika saboda littafin da ya rubuta mai taken "Things Fall Apart," wanda ke da jigon yadda bakaken fata suka sha wahala ga turawan mulkin mallaka a karni na 1800.

Chinua Achebe, marubuci a Najeriya ya mutu
Chinua Achebe, marubuci a Najeriya ya mutu Reuters
Talla

Chinua Achebe, ya mutu ne a wata asibiti a Massachusetts kasar Amurka. Kamar yadda Mari Yamazaki kakakin kamfanin buga littafi na Penguin ta tabbatarwa kamfanin Dillacin Labaran Faransa AFP.

Achebe ya yi fice ne a duniya saboda Littafinsa da ya rubuta mai taken "Things Fall Apart," wanda ke bayani game da yadda Turawan Ingila suka yi mulkin Mallaka da kuma al’adun kabilar shi ta Igbo a kudancin Najeriya.

Achebe ya dade yana adawa da matsalar cin hanci da rashawa a Najeriya, lamarin da ya gurgunta tattalin arzikin kasar.

Amma Achebe ya goyi bayan yakin Biafra na Kabilar Igbo da ya lakume rayukan mutane kusan Miliyan a shekarar 1967-1970 a lokacin da suka nemi ballewa daga Najeriya.

A shekarar 2011 Achebe ya yi watsi da lambar yabon da gwamnatin Najeriya za ta ba shi wanda shi ne karo na biyu.

Achebe ya kwashe shekaru da dama a kasar Amurka a matsayin Farfesa a Jami’ar Brown a Rhode Island.

Wata marubuciyar Afrika ta Kudu ta bayyana Achebe a matsayin Uban Adabi a Afrika a lokacin da zai karbi wata kayutar Adabi ta Duniya.

Yana da wahala Dalibin sashen Turanci ya kammala karatu ba tare da ya karanta littafin Achebe ba, musamman a Najeriya.

Sai dai kuma Achebe bai taba lashe kyautar Nobel ba a fannin adabi kamar yadda Wole Soyinka,ya lashe kyautar a shekarar 1986.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.