Isa ga babban shafi

Newcastel ta fita daga gasar Zakarun nahiyar Turai a matakin rukuni

Damawa da ake yi da Newcastle United a gasar Zakarun nahiyar Turai ya kawo karshe a daren Laraba, bayan da AcMilan ta taso daga baya ta samu nasara a kanta a  filinta na St James' Park.

Kocin Newcastle United Eddie Howe
Kocin Newcastle United Eddie Howe Action Images via Reuters - Lee Smith
Talla

Newcastle ta yi mafarakin ganin kanta a zagayen sili daya kwale ne tun bayan da Joelinton ya saka kwallo a ragar Milan a minti na 33, a yayin da a daidai lokacin  Borussia Dortmund ke kan gaba a wasan da take fafatwa da Paris St-Germain a Jamus.

Idan da wasannin na Jamus da Ingila sun kare a haka, Newcastle za ta haye, bisa yadda take kan gaba a dukkan karawar da ta yi da PSG, amma sai lammura suka sauya a cikin ‘yan mintoci, kafin a kai sa’a guda da ilharin wasannin, inda matashi Warren Zaire-Emery ya farke wa PSG kwallo a Jamus, a yayin da tsohon dan wasan Chelsea, Christian Pulisic ya farke wa AC Milan a Ingila.

Saura minti 6 a Karkare wasan ne aka tantance makomar  Newcastle, sakamkon kwallon da dan wasan Najeriya, wanda ya shigo wa Milan daga baya, Samuel Chukwueze ya saka mata, wasa ya tashi 2 da 1.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.