Isa ga babban shafi

PSV Eindhoven daga Netherland, ta doke Lens a gasar zakarun Turai

A gasar cin kofin zakarun Turai, a karo na farko kungiyar kwallon kafar Lens ta kasar Faransa ta yi kasa a gwiwa yayin fafatawa da kungiyar PSV Eindhoven daga kasar Netherland, wacce ta doke Lens da ci  1 da nema.Dan wasan kungiyar PSV Eindhoven Luuk de Jong mai shekaru 33 ne zura kwallo a ragar ta Lens vayan mituna 12.

Kofin gasar zakarun Turai
Kofin gasar zakarun Turai REUTERS - MASSIMO PINCA
Talla

Baya ga wannan wasa,mu sanar da masu sauraren mu cewa Real Madrid,Real Sociedad,Inter Milan,Bayern Munich sun samu tikitin su na kasancewa a mataki na gaba a wanan gasar cin kofin zakarun Turai.

A rukunin farko ko rukunin A.

Fc Copenhague ta doke Manchesterd United da ci 4 da 3,yayinda Bayern Munich ta doke Galatasaray da ci 2 da 1.

Kofin gasar zakarun Turai
Kofin gasar zakarun Turai REUTERS - MASSIMO PINCA

Ranar 29 ga wannan watan da muke cikin sa Galatasarai da Manchesterd United za su haduwa.

A rukuni Ba, Arsenal ta doke Sevilla da ci 2 da nema,kuma kamar dai yada aka ji PSV Heidhoven ta doke  Lens da ci 1 mai ban haushi.

Jude Bellingham
Jude Bellingham © LUSA - HUGO DELGADO

A rukunnin na uku ko rukunnin C Naples daga Italia ta yi kunen doki da Union Berlin daga Jamus 1 da 1.

Sporting Braga ba ta ji da dadi ba bayan karawa da Real Madrid,wacce ta doke ta da ci 3 da nema.

A rukunni Da ko rukuni na hudum,Real Sociedad ta doke Benfica da ci 3 da 1.Sai Inter Milan da ta lalasa Salzbourg da ci 1 mai ban haushi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.