Ban yi alkawarin lashe kofin nahiyar Afrika a 2019 ba - Rohr
Mai horar da tawagar kwallon kafar Najeriya ta Super Eagles Gernot Rohr, ya ce ba zai iya yin alkawarin lashe kofin gasar kwallon kafa ta kasashen Afrika ba, da Kamaru za ta karbi bakunci a shekarar 2019.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
A halin da ake ciki, Najeriya ce ke jagorantar, rukuni na biyar da take ciki, a wasannin neman cancantar halartar gasar cin kofin nahiyar Afrika da maki 9, yayinda Afrika ta Kudu ke mataki na biyu da maki 7. Kasashen Libya da Seychelles ke mataki na 3 da na 4 a rukunin.
A ranar 17 ga watan Nuwamba mai zuwa Najeriya zata yi tattaki zuwa birnin Johannesburg domin fafatawa da Afrika ta Kudu, wanda muddin ta lashe wasan, kai tsaye za ta samu tikitin halartar gasar cin kofin ta nahiyar Afrika.
A wasanni biyu da ta fafata na neman cancantar Najeriya ta lallasa Libya da kwallaye 4-0 a zagayen farko, zalika ta sake nasarar doke ta da kwallaye 3-2 a zagaye na biyu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu