PSG na fatan lallasa Real Madrid duk da rashin Neymar
Kungiyar kwallon kafa ta PSG da ke Faransa na ci gaba da fatan lallasa takwararta RealMadrid a gobe Talata, wasan da ta ke fatan kafa tarihi da shi duk kuwa da rashin tsadadden dan wasanta Neymar Dos Santos.
Wallafawa ranar:
A cewar kochin kungiyar Unai Emery, sun dukkanin shirin da ya kamata don tunkarar wasan a gobe, yana mai cewa bai je paris kawai don ya karbi kudi ba, a a yaje ne don ya kafa tarihi ta yadda zai kai Club din matsayin da bai taba zuwa ba.
Emery ya ce yin kafada-da-kafada tsakaninsu da manyan Club irin su Real Madrid ne za su nunawa duniya irin karfin da kuma horon da ‘yan wasansu su ke da shi.
A watan daya gabata ne dai Neymar ya samu rauni a gwiwarsa matakin da babanshi ya ce yana bukatar makwanni shidda kafin murmurewa.
Ko a wancan karon ma dai, yayin haduwar Real Madrid da PSG, Real din ce ta lallasa PSG da ci 3 da 1.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu