Buhari ya bada umarnin biyan Super Falcons
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bada umarnin gaggauta biyan ‘yan wasan Super Falcons kudadensu da su ke bin hukumar kwallonn kafar kasar.
Wallafawa ranar:
Wannan na zuwa ne bayan zanga-zangar da kungiyar ta mata ta gudanar a majalisar tarayyar kasar don nuna bacin ransu da rashin biyansu kudin nasu bayan sun lashe gasar cin kofin Afrika ta mata a Kamaru.
‘Yan wasan sun yi zanga-zangar ce don janyo hankalin shugaba Buhari da ya halarci majalisar a jiya don gabatar da daftarin kasafin kudin shekara mai zuwa.
Tuni dai matan suka koma Otel din Agura bayan an yi musu alkawarin biyan su hakkokinsu.
Kowacce daga cikinsu na bukatar karbar kimanin Dala dubu 23 da 650 kwatankwacin Naira miliyan 11 na Naira.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu