FA ta ci tarar Chelsea da Manchester City
Hukumar kwallon kafar Ingila ta ci tarar Chelsea da Manchester City bayan ‘yan wasan kungiyoyin biyu sun tada hatsaniya a fafatawar da suka yi a Etihad a farkon wannan watan a gasar Premeir.
Wallafawa ranar:
Hatsaniyar ta kaure ne a karshen wasan wanda Chelsea ta samu nasara da ci 3-1 a kan Manchester City, bayan an kori Sergio Aguero na City daga fili sakamakon harin da ya kai wa David Luiz.
Sannan kuma alkalin wasan ya sake korar Fernandinho na Man City saboda samun sa da laifin cukume Cesc Fabregas.
Yanzu haka dai Chesea za ta biya tarar Pam dubu 100 yayin da Manchester City za ta biya Pam dubu 35.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu